YADDA AKA SHIRYA KASHE TINUBU, KASHIM SHETTIMA, AKPABIO, TAJUDDEEN ABBAS DA WASU MANYAN KASAR NAJERIYA : Sojojin da ake zargi da shirin juyin mulki sun yi niyyar hallaka manyan jami’an gwamnati
Wasu majiyoyin tsaro sun bayyana cewa jami’an sojan da ake zargi da shirin juyin mulki a Najeriya sun tsara kai hari da kuma kashe manyan jami’an gwamnati, ciki har da shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, da mataimakinsa, Kashim Shettima, da wasu shugabanni na majalisa.
Majiyoyin sun shaida wa jaridar Premium Times cewa shirin ya haÉa da kai hari a lokaci guda ga waÉanda aka nufa, a ranar da dukkan su za su kasance cikin Ęasa.
“Sun tsara su hallaka su duka a lokaci guda. Suna neman lokaci da za su tabbata duk manyan jami’an nan suna cikin Ęasa. A duk inda suke, za a kashe su,” in ji wata majiya.
Rahoton ya Ęara da cewa waÉanda ake zargi sun kuma yi niyyar kama wasu manyan jami’an tsaro ciki har da shugabannin rundunonin soja.
“Haka kuma sun tsara su kama manyan hafsoshin soja, ciki har da shugabannin rundunoni, amma ba su da niyyar kashe su,” in ji wata majiya daga cikin binciken.
Rahoton ya ce sunan waÉanda aka nufa da kisan ya haÉa da:
* Shugaban Ęasa Bola Ahmed Tinubu
* Mataimakin shugaban Ęasa Kashim Shettima
* Shugaban majalisar dattawa Godswill Akpabio
* Shugaban majalisar wakilai Tajudeen Abbas
An ce waÉanda ake zargi sun samu taimako daga wasu jami’an da ke aiki a fadar shugaban Ęasa da wasu wurare masu muhimmanci don tattara bayanai game da motsin waÉanda ake son kai wa hari.
A wata sanarwa da rundunar sojojin ta fitar, an bayyana cewa binciken da ake yi bai tabbatar da wani yunkurin juyin mulki ba tukuna, amma ana duba yiwuwar take dokoki da rashin ladabi daga jami’an da ake zargi.
Rahoton ya ce wannan lamari ya haifar da damuwa a tsakanin hukumomin tsaro da gwamnati, inda ake ganin shi ne daya daga cikin dalilan da ya sa aka dakatar da bikin ranar ’yancin kai ta bana.
Rundunar sojojin Najeriya ta bayyana cewa tana ci gaba da bincike kan lamarin, tare da tabbatar da cewa ba za ta lamunci duk wani yunkuri da zai barazana ga tsarin dimokuraÉiyya da zaman lafiya a Ęasar ba.
A WATA MAJIYAR!!! šš½
ta gano cewa Jami'an soja da aka tsare bisa zargin yunkurin kifar da Gwamnatin Shugaba Bola Tinubu, na aiki ne a karkashin ofishin mai ba wa Shugaban kasa shawara akan harkokin tsaro.
Wanda ke rike da Ofishin a halin yanzu shi ne Nuhu Ribadu, wanda ke aiki a matsayin mai ba wa Shugaban kasa shawara akan harkokin tsaro.
Akasari ana zakulo ma'aikatan ofishin daga hukumar tara bayanan sirri ta Najeriya, Rundunar Soja, da sauran hukumomin tabbatar da tsaro.
Duk da karyata yunkurin juyin mulkin da Rundunar sojin ta yi, a karin haske da ya yi wa majiyar mu a yammacin Asabar,, wani babban jami'in sashin tara bayanan sirri na rundunar Sojin, ya ce sojojin wadanda mafiya yawan su 'yan Arewa Ne, suna aiki da Ofishin mai ba wa Shugaban kasa shawara akan harkokin tsaro.
Ya bayyana sunan daya daga cikin jagororin kitsa yunkurin juyin mulkin a matsayin Laftanal Kanar Al-Makura, wanda bai jima da dawowa ba daga samun horon kwarewar aiki a kasar China.
An Kama Janar da Wasu Manyan Sojoji Bisa Zargin Shirya Juyin Mulki ga Shugaba Tinubu
Rahotannin daga Sahara Reporters sun bayyana cewa Hukumar Tsaron Ęasa ta Najeriya (Defence Intelligence Agency – DIA) ta kama Janar din na Rundunar Soja tare da wasu manyan jami’an soja 15 bisa zargin shirya juyin mulki domin kifar da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
Wata majiya daga cikin hukumar ta tabbatar da cewa jami’an, waÉanda ke daga matakin Captain zuwa Brigadier-General, sun fara gudanar da tarurruka na sirri da nufin kifar da gwamnati saboda abin da suka kira “cin hanci da rashawa da son kai a cikin siyasar Ęasar”.
A cewar majiyar: “Wadannan jami’an sojoji suna shirin juyin mulki ne don su kifar da gwamnatin Shugaba Tinubu da sauran manyan ‘yan siyasa. Hukumar tsaro ta gano shirin tun kafin su aiwatar da shi, ta kuma kama su a gidajensu daban-daban a fadin Ęasar.”
A baya, rundunar sojin Najeriya ta fitar da wata sanarwa inda ta ce an kama jami’an ne bisa laifin “rashawa da rashin ladabi da karya Ęa’idojin aiki”, tana mai cewa wasu daga cikinsu sun kasa samun karin girma saboda “gazawa a jarabawar karin matsayi”.
Sai dai majiyoyin tsaro sun bayyana cewa wannan sanarwa ba cikakkiya ba ce, domin a zahiri an kama su ne saboda zargin juyin mulki.
Wani babban jami’in tsaro ya ce bikin ranar ‘yancin kai na watan Oktoba 1, 2025 an soke shi saboda tsoron cewa shirin juyin mulkin zai gudana a wannan lokacin.
“Rahotannin sirri sun nuna cewa sun shirya harin juyin mulki ne a lokacin baje kolin Soja na ranar 1 ga Oktoba, inda za su bude wuta kan Shugaban Ęasa da sauran jami’an gwamnati. Wannan ne ya sa aka soke baje kolin domin kare rayukan manyan shugabannin kasar.”
A halin yanzu, jami’an 16 Éin na ci gaba da fuskantar tsarewa a hedikwatar Defence Intelligence Agency (DIA) da ke Abuja, yayin da ake ci gaba da gudanar da bincike a kansu.
Tun bayan samun ‘yancin kai a 1960, Najeriya ta fuskanci juyin mulki guda biyar da suka yi nasara, inda duka suka haifar da sauye-sauyen mulki a cikin tarihi.

0 Comments
Ku Fadi Ra'ayinku