An ga jinjirin watan sallah a Najeriya

KDK Hausa

Mai Alfarma Sarkin Musulmi kuma shugaban al’ummar Musulmin Najeriya, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar, ya bayyana ranar Alhamis 20 ga Afrilu, 2023 daidai da 29 ga watan Ramadan 1444 bayan hijira a matsayin karshen azumin watan Ramadan na shekara.

 Ma’ana, gobe Juma’a 21 ga Afrilu daidai da 1 ga Shawwal ita ce Idin Alfijir, in ji shi.

 Sultan Abubakar, yayin da yake bayyana hakan a fadarsa ranar Alhamis, ya ce an ga watan a sassan Najeriya kuma kwamitin ganin wata na kasa ya tabbatar da ganin watan.

Domin karin bayani danna 👉 WANNAN 

0 Comments

Ku Fadi Ra'ayinku