ADAMAWA FINTIRI YA KAYAR DA BINANI INJI INEC

KDK Hausa


ADAMAWA FINTIRI YA KAYAR DA BINANI INJI INEC


Hukumar zaÉ“e INEC ta sanar da Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri a matsayin wanda ya lashe zaÉ“en jihar Adamawa, wanda ya Æ™are cikin Takaddama da sarkakiyya. 

Jami'in sanar da sakamakon zaɓen gwamna na Adamawa, Farfesa Mohammed Mele ya ce Ahmadu Fintiri ya yi nasarar lashe zaɓen ne da ƙuri'a, 430, 861.

Gwamnan mai ci ya samu nasara a kan babbar abokiyar fafatawarsa Aisha Ɗahiru Binani wadda ta samu ƙuri'a, 398, 788.

Wannan nasara ta bai wa Fintiri ikon ci gaba da mulkin jihar Adamawa a wa'adi na biyu. Kamar yadda hukumar zabe mai zaman kanta INEC ta tabbatar yau Talata.

Domin karin bayani danna 👉 WANNAN 

0 Comments

Ku Fadi Ra'ayinku